Gafarta Wa Waɗansu

Derek Prince
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
Hanya guda da Masu Bi ke ba wa Shaiɗan dama a rayuwarsu ita ce ta wurin rashin gafartawa wasu. Yesu ya koya mana cewa Allah yana gafarta mana daidai gwargwadon yadda mu ke gafartawa wasu. Ya ce:
“Domin in kun yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku na sama ma zai yafe muku. In kuwa ba ku yafe wa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku laifofinku ba” (Matta 6:14–15)
Ba mu da haƙƙi ko damar mu nemi gafara daga wurin Allah fiye da yadda muke gafarta wa wasu. Idan akwai wani mutum wanda ba mu gafarta masa ba, gwargwadon haka, ba za mu sami gafara daga wurin Allah ba. Wannan yana nufin inda muke da rashin gafartawa a rayuwarmu, wannan wurin ne Shaiɗan har yanzu ke da damar mallaka. Ba za mu iya fitar da shi ba sai mun gafarta wa duk wanda ya kamata a gafarta masa.
Fansa na tafiya tare da gafarar zunubai. Idan an gafarta mana duk zunubanmu, to, muna da cikakkun haƙƙin fansa. Shaiɗan ba shi da wani haƙƙi na bisa doka da ya rage a kanmu. Amma idan akwai wani ɓangare a rayuwarmu inda zunubi ke mallaka,to, Shaiɗan har yanzu yana da haƙƙi na bisa doka a wannan ɓangaren. Ko mun tara duk masu wa’azi na duniya su yi mana wa’azi, sa’annan suyi addu’a a kan mu, ba za mu kawar da shaiɗan ba, domin ya san yana da haƙƙi na bisa doka. Kada mu manta da cewa shaiɗan gwani ne na doka. Shi ma ya san haka. Amma duk da haka, Maganar Allah tana ba mu cikakkiyar gafarar zunubi gaba ɗaya. Yana da muhimmanci mu riƙe wannan cikakkiyar gafarar, ka da mu bar wani laifin da ba mu gafarta ba.
*Prayer Response
Lambar: WD-B097-050-HAU