Sauraron Muryar Allah

Derek Prince
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
Makomar mu, na alheri ko na mugunta, ya danganta ne ga muryar da muka zaɓa mu saurara. Sauraron muryar Ubangiji da yin biyayya ga abin da ya ce zai kawo albarka. Yin watsi da muryar Ubangiji zai kawo la'anoni da yawa. Ba shi yiwuwa a yi ma Allah biyayya ba tare da fara jin muryarsa ba, domin muryarsa ce ke gaya mana abin da yake buƙata daga gare mu.
Yawancin waɗanda ke kiran kansu Krista ba sa maida hankali ga sauraren muryar Allah. Muna iya ci gaba da ayyukan mu na addini, amma abubuwa ne waɗanda mu ka saba yi kawai—tsare tsaren da muka sa wa kanmu wanɗanda muna yi ne kawai ba don mun ji muryar Ubangiji ba. A kowane zamani, Allah yana buƙatar mutanensa su saurari muryar sa.
A cikin Irmiya 7, Allah ya bayyana ainihin abin da yake buƙata daga Isra'ila lokacin da ya fanshe su daga Ƙasar Masar. Abu na farko da yake da shi a zuciya ba shine kiyaye Doka don miƙa haɗayu ba ne, amma sauraron muryar sa. Muryar sa ce za ta jagorance su su kiyaye Doka kuma su ba da haɗayun da ake buƙata. Kiyaye abin da Doka ta ce ba shi da amfani idan ba su yi haka ba sakamakon jin muryar Ubangiji. Babban abin da Allah yake buƙata shi ne mu saurari muryarsa.
“A ranar da na fito da kakanninku daga ƙasar Masar, ban yi magana da su, ko na umarce su, akan hadayun ƙonawa ko na sadaka ba. Amma wannan ne abin da na umurce su, cewa, ‘Ku yi biyayya ga muryata, kuma ni zan zama Allahnku, kuma ku za ku zama mutanena.’” (Irmiya 7:22–23)
Buƙata mafi sauƙi ita ce, “Ku yi biyayya da muryata, ni kuma zan zama Allahnku.” Wannan shi ne yadda aka taƙaita shi a sauƙaƙe.
*Prayer Response
Lambar: WD-B097-046-HAU