Jikina: Haikalin Ubangiji

Derek Prince
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
“Duk da haka, Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda annabi Ishaya ya ce, Allah ya ce, ‘Sama ita ce kursiyina, ƙasa kuwa matashin ƙafa ta. Wane wuri kuma za ku gina mani? Ko kuwa wane wuri ne wurin hutu na? Ba da iko na na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?’” (Ayyukan Manzanni 7:48–50)
Allah na zaune a cikin haikalin da ba hannu ya yi ba, amma gini ne na Allah bisa ga nufin Sa. Wannan haikalin shi ne jikin Mai Bi, wanda aka fansa da jinin Yesu Almasihu. Kamar yadda Bulus ya bayyana a 1 Korinthiyawa 6:13:
“Abinci don ciki aka yi shi, ciki kuma don abinci, Allah kuma zai hallaka duka biyu, wannan da wancan. Jiki kam, ba don fasikanci ya ke ba, sai dai domin Ubangiji, kuma Ubangiji domin jiki.”
Wannan ayar tana magana ne game da abinci domin ciki, da kuma ciki domin abinci. A cikin Misalai, an ce:
“Mai adalci ya kan ci har ransa ya ƙoshi.” (Misalai 13:25)
Mu masu adalci ba ma cin abinci fiye da kima. Me ya sa? Domin jikunan mu haikalin Ubangiji ne, kuma bai kamata mu ƙazantar da su ta hanyar cin abinci da haɗama, ko shan giya, ko aikata alfasha, ko kowane irin abinda bai dace ba. Jiki na Ubangiji ne, kuma Ubangiji domin jiki ne. Sa’ad da na ba Ubangiji jiki na, to, ina da haƙƙi na Ubangiji a kan jikina.
Bari mu yi amfani da wannan misalin: Idan na sayi wani gida, ni ke da alhakin kula da shi; amma idan ina zaune a gidan haya, mai gidan hayar ne ke da hakkin kula da shi. Idan damar da muka ba Yesu a kan jikunan mu na ɗan lokaci ne, to, ba zai ɗauki hakkin kula da su ba. Amma idan Shi ne mai mallakar jikkunan mu, to, Shi ne ke da alhakin kula da su. Wannan ce irin dangantakar da yake so da mu.
*Prayer Response
Lambar: WD-B097-044-HAU