Shaida Zunubin Mu

Derek Prince
Kamar
Raba
Hausa
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
A cikin Zabura 32, Sarki Dauda ya rubuta daga abin da ya faru da shi:
“Sa’ad da na yi shiru, Kasusuwa na sun bushe saboda nishi na dukan yini, Gama dare da rana hannun ka ya yi nauyi a kaina, Ƙarfi na ya ƙare sarai kamar a zafin rani. Sa'an nan na shaida maka zunubina, Ban kuwa ɓoye mugunta ta ba, Na ce, ‘Zan faɗa wa Ubangiji laifofina,’—kai kuma ka gafarta mini zunubina. (ayoyi 3-5)
Na gaskata cewa sa'ad da Dauda ya rubuta wannan, ya na tune da batun Barsheba, matar Uriya Bahitte. Wannan mummunan yanayi ne da Dauda ya yi zina, sannan ya yi kisa don ya ɓoye zinarsa. Babu shakka Dauda ya kasance kamar yawancin mu. Ya daɗe yana ƙi ya fuskanci gaskiyar zunubinsa. Ya yi ƙoƙari ya yi watsi da shi.
A cikin ayoyi na gaba, Dauda ya nuna yadda za mu yi:
“Domin wannan kowane mai tsoron Allah shi yi addu’a gare ka, lokacin da ka ke samuwa, Hakika, sa’ad da ruwaye masu zurfi suka yi rigyawa, ba za su kai gare shi ba, Kai ne mafaka ta, za ka tsare ni daga wahala, Ka kewaye ni da waƙoƙi na ceto.”
(ayoyi 6-7)
Ba a makara wurin furta zunuban mu ga Allah da neman mafaka a cikin cetonsa. Zai kuɓutar da mu da ga zunuban mu idan za mu shaida su kuma mu tuba.
*Prayer Response
Ubangiji, na gode saboda jinin Yesu. Ina furta cewa domin na shaida kowane zunubi da na yi ƙoƙari in ɓoye, Ka gafarta laifin zunubina. Ka kiyaye ni daga wahala, Ka kewaye ni da ceto. Ta wurin jinin Yesu, an gafarta mani dukan zunubai na. Amin.
Nayi Sallah
Kamar
Raba
Expand Content
Lambar: WD-B097-020-HAU
Gabatar da martani