Daidaita Hujjoji Duka

Derek Prince
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
Idan an gafarta mana dukan zunuban mu, muna da cikakkun albarku na fansa. Amma idan akwai wani zunubi a rayuwar mu da ba mu furta ba - kuma ba a gafarta mana ba - ba mu da cikakkun albarku na fansa a wannan wurin. Har yanzu Shaiɗan na da mariƙa a wannan wurin. Na tabbatar da hakan sau da yawa a cikin hidimar ‘yantarwa. Idan Shaidan yana da wata mariƙa, to, ba zai ƙyale ba. Za ka iya yin ihu a fuskarsa ko kuma ka yi azumi na mako ɗaya, amma ba za ka taɓa canza yanayin ba domin Shaidan ya san yana da wata mariƙa wadda har yanzu ba a warware ta ba.
Wata hanya mafi yawa da Masu Bi ke ba Shaidan dama a rayuwarsu ita ce ta rashin gafartawa wasu. Yesu ya koya mana cewa Allah yana gafarta mana kamar yadda muke gafarta wa wasu. Za mu yi addu'a:
“Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda muke gafarta wa waɗanda suke yi mana laifi” (Matta 6:12)
Ba mu cancanci mu nemi gafarar Allah fiye da yadda mu ke gafarta wa waɗansu ba (dubi aya ta 14-15). Don haka, idan akwai mutanen da ba mu gafarta ma su ba, a daidai haka, Allah ma ba zai gafarta mana ba. Wato, duk wani wurin da ba mu gafarta a rayuwar mu ba, wannan wurin ne da har yanzu Shaidan ya ke riƙewa. Ka yi duk abin da za ka yi; ba za ka taɓa iya kawar da shi ba har sai ka gafarta wa wanda ka ke buƙatar gafartawa.
*Prayer Response
Lambar: WD-B097-016-HAU