Canza wuri Mai Amfani

Derek Prince
*Last Updated: March 2026
2 min read
This teaching is not currently available in Hausa.
“Bari fansassu na Ubangiji su faɗi hakanan, Wanɗanda ya fanshe su daga hannun magabci.” (Zabura 107:2)
Wasu mutane na iya sanin cewa an fanshe su daga hannun shaiɗan; wasu ba su sani ba. Amma na san sarai inda nake a da kafin shigowar Yesu a cikin rayuwa ta; ba ni da shakka game da wannan. Na san yadda zama a hannun shaiɗan ta ke, kuma ba zan so in sa ke kasancewa a wurin ba. Na kuma sani, ta wurin abin da Maganar Allah ta ce, cewa jinin Yesu ne ya fitar da ni daga hannun shaiɗan zuwa hannun Makiyayi Mai Kyau. Yesu ya ce game da mutanensa:
“Ina ba su rai na har abada; ba kuwa za su lalace ba daɗai, ba kuwa wanda zai ƙwace su daga hannuna.”
(Yohanna 10:28)
Wannan shi ne canjawa daga hannun shaidan zuwa hannun Ubangiji.
Amma lura cewa wannan canja wuri yana da tasiri kuma zai amfane mu ne kawai idan muka yi abu ɗaya: Idan muka “faɗi haka.” “Bari waɗanda Ubangiji ya fanshe su su faɗi haka.” Idan an fanshe ku, ku faɗi! Idan ba ku fada ba, fansar ku ba za ta amfane ku ba. Kalmar shaidarka ita ce ke sa jinin ya yi maka amfani.
*Prayer Response
Lambar: WD-B097-010-HAU